Wanda Ya kyautata kowane abu da ya halicce shi; kuma Ya fari halittar mutum daga tavo(7- AS-SAJDAH)
Nuna katika
Lalle a cikin halittar sammai da qasa da sassavawar dare da rana, tabbas akwai ayoyi ga ma’abota hankula(ĀLI ‘IMRĀN-190)
Da kuma cikin kawunanku. Yanzu ba kwa lura ba?
Ya halicci mutum daga busasshen tavo kamar kasko
Sannan idan aka gama salla sai ku bazu a bayan qasa ku kuma nema daga falalar Allah, kuma ku ambaci Allah da yawa don ku rabauta(AL‑JUMU‘AH-10)
Haqiqa Mun girmama ‘yan’adam, Muka kuma xauke su (kan ababen hawa) na sarari da na ruwa, Muka kuma arzuta su daga tsarkakan (abubuwa) kuma Muka fifita su a kan wasu da yawa daga abin da Muka halitta nesa ba kusa ba
Ya ku mutane, ku kiyaye dokokin Ubangijinku Wanda Ya halicce ku daga rai guda xaya, kuma Ya halicci matarsa daga shi, kuma Ya yaxa maza da mata masu yawa daga gare su. Kuma ku kiyaye dokokin Allah Wanda kuke yi wa juna magiya da Shi, kuma ku kiyaye (yanke) zumunci. Lalle Allah Mai kula da ku ne