Sannan bayansu Muka mayar da ku madadinsu a bayan qasa don Mu ga me za ku aikata
Nuna katika
Ba a bayar da Aljannar Firdaus sai ga wanda yayi imani yayi ayyuka nagari. Sakamako ne wanda ba za a iya kwatanta shi da dukiya ko matsayi ba. Lalle ita (Firdausi) Aljanna ce ta dawwama ga wanda ya kasance a kan tafarki ingantacce. #Aljannar_Firdaus
Jiragen ruwa da suke gudu a cikin kogi, tunatarwa ce garemu game da girman Allah, wanda ya hore mana komai a wannan duniyar. Mu gode wa Allah bisa ni’imominsa wadanda ba za su lissafu ba, ba kuma za su qididdigu ba. #Gode wa_Allah
Don haka sai ka tsaya totar kamar yadda aka umarce ka kai da waxanda suka tuba tare da kai, kada kuwa ku wuce iyaka. Lalle Shi (Allah) Mai ganin abin da kuke aikatawa ne
Lalle Mun bijiro da amana ga sammai da qasa da duwatsu sai suka qi xaukar ta suka ji tsoron ta, sai kuwa mutum ya xauke ta; lalle shi (mutum) ya kasance mai zaluntar kansa ne, mai jahilci
Ka yi tuntuntuni game da girman amana wadda sammai da kasa da duwatsu suka ki yarda su dauketa...amma a haka mutum ya karbeta, sai dai shi mai yawan zalintar kansa ne, mai yawan jahiltar karshen lamarinsa ne. #Tuntuntuni #Alqur’ani.
Allah ne wanda Ya hore muku kogi don jiragen ruwa su riqa gudu a cikinsa da umarninsa, don kuma ku nema daga falalarsa don kuma ku godeYa kuma hore muku abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa gaba xayansu daga gare Shi. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga mutanen da suke yin tunani