Sannan bayansu Muka mayar da ku madadinsu a bayan qasa don Mu ga me za ku aikata
Nuna katika
Wanda ya yi kyakkyawan aiki namiji ko mace alhali shi yana mumini, to lalle za Mu raya shi rayuwa mai daxi, kuma za Mu saka musu ladansu da mafi kyan abin da suka kasance suna aikatawa
Amana nauyi ne mai girma da Allah ya bijirar dashi ga manyan halittu, amma suka ki yarda su karba, amma dan’adam yayi jara’a ya dauketa! Shin mun san kuwa hakikanin amanar da muka dauka a wuyayanmu? #Amana#
Kuma ka tuna sa’adda Ubangijinka Ya ce da mala’iku: “Lalle ni zan sanya wani halifa a bayan qasa.” Suka ce: “Yanzu za Ka sanya mata wanda zai yi varna a cikinta kuma ya zubar da jini, alhali ga mu muna tasbihi tare da gode Maka, kuma muna tsarkake Ka?” (Allah) Ya ce: “Ni fa tabbas Na san abin da ku ba ku sani ba.”
Ha’inci yana yin suka ga amincin da aka yi wa mutum, yana kuma karya zukata, yana kuma zubar da kwarjini. Kada ka yi ha’inci cikin abin da aka dora maka nauyinsa, don kowace amana watarana za a tambayeka game da ita. #Tsaftace-Niyya
Allah ne wanda Ya hore muku kogi don jiragen ruwa su riqa gudu a cikinsa da umarninsa, don kuma ku nema daga falalarsa don kuma ku godeYa kuma hore muku abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa gaba xayansu daga gare Shi. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga mutanen da suke yin tunani
Lalle Mun bijiro da amana ga sammai da qasa da duwatsu sai suka qi xaukar ta suka ji tsoron ta, sai kuwa mutum ya xauke ta; lalle shi (mutum) ya kasance mai zaluntar kansa ne, mai jahilci