Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki na gari, to (Allah) Mai rahama zai sanya musu qauna
Nuna katika
Ya ku waxanda suka yi imani, duk wanda ya yi ridda daga cikinku, ya bar addininsa, to (ya sani) Allah zai kawo waxansu mutane da Yake son su suna son Sa, suna masu qasqantar da kai ga muminai, suna masu nuna wa kafirai isa, suna yin jihadi don xaukaka kalmar Allah, kuma ba sa jin tsoron zargin wani mai zargi. Wannan falalar Allah ce da Yake bayar d...
Ya ku mutane, haqiqa gargaxi ya zo muku daga Ubangijinku da kuma waraka ga abin da yake cikin zukatanku, kuma shiriya ne da rahama ga muminai
“Lalle ni kam na juyar da fuskata ga Wanda Ya halicci sammai da qasa, ina mai kauce wa varna kuma ni ba na cikin masu yin shirka.”
Yayin da zuciya ta cika da son Allah, dukkan wasu abubuwa da ake so za su zama ba wani abu ba, kuma ma’auni zai daidaita. #Son_Allah
A duniyar da take cakuxe da duhu, Alqur’ani yana zuwa a matsayin wani haske da zai daidaita maka lamarinka, ba ma haka ba, sai ya nuna maka hanyar da za ka bi ka samu aminci. #Hanyoyin_Aminci
Babu wata buqata da zuciya take da ita face Alqur’ani ya yi bayani game da ita ko kuma ya ba da wata shiriya ko ya kawo rahama game da ita. #Shiriya_Da Rahama.