Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki na gari, to (Allah) Mai rahama zai sanya musu qauna
Nuna katika
Ya ku waxanda aka bai wa Littafi, haqiqa Manzonmu ya zo muku, yana bayyana muku da yawa daga cikin abin da kuke voyewa daga Littafin, yana kuma yin afuwa ga abubuwa da dama daga ciki. Haqiqa haske ya zo muku daga Allah, da kuma Littafi mai bayyanawaDa shi ne Allah Yake shiryar da wanda ya bi yardarsa hanyoyi na aminci, kuma Yake fitar da su daga du...
Alqur’ani ba ya barinka a tsakiyar hanya, sai dai yana kasancewa tare da kai har sai ka samu nutsuwa. #Nutsuwar_Alqur’ani.
Kuma akwai wasu mutane waxanda suke bauta wa wasu kishiyoyi ba Allah ba; suna son su kamar son Allah; waxanda kuwa suka yi imani sun fi son Allah (fiye da komai). Da a ce waxanda suka yi zalunci za su ga lokacin da suke ido huxu da azaba (to da sun gane) cewa, lalle duk wani qarfi na Allah ne gaba xaya, kuma lalle Allah Mai tsananin azaba ne
Shiriya za ta iya zuwa ba zato ba tsammani, sannan kuma za ta iya canja dukkan wani abu da zai zo a bayanta. #Hasken_Imani
Ya ku mutane, haqiqa gargaxi ya zo muku daga Ubangijinku da kuma waraka ga abin da yake cikin zukatanku, kuma shiriya ne da rahama ga muminai
Yayin da tambayoyi suka yi cincirindo, to ba ka buqatar hayaniya a lokacin, sai dai kana buqatar hasken da zai yi maka jagora cikin nutsuwa. #Hanyar_Gaskiya