(Allah) Mai rahama.
Shi Ya koyar da Alqur’ani.
Ya halicci mutum .
Ya koyar da shi bayani.
Nuna katika
Ba a yawaita magana yayin da ake cikin musiba, Ya isheka ka yi ta nanata fadin: “mu na Allah ne, kuma zuwa gare shi za mu koma” a cikin ranka. Domin a cikin fadar hakan akwai, mika wuya da yarda da kuma nutsuwa. #Mika wuya_da komawa.
(Su ne) waxanda idan wata musiba ta same su sai su ce: “Lalle mu na Allah ne, kuma lalle mu gare Shi muke komawa.”
Gafala tana kekasar da zukata Ambaton Allah kuma yana tausasata ya kuma sa ta yin sabuwar rayuwa. Kada ka bari duniya ta tafiyar da kai_ka dawo yanzu-yanzu. Komawa_Zuwa ga_Allah
Ana karanta Alkur’ani ne don a tsarkake rai Salla kuma ana tsayar da ita ne don ta tsarkake yanayin mutum Duk wanda ya kiyaye wurin yi wa Ubangijinsa salla, to za ta tsare shi daga karkacewa. #Tasirin_Salla
Ka karanta abin da ake yi maka wahayinsa na Alqur’ani, ka kuma tsai da salla; lalle salla tana hana alfasha da kuma abin qi. Kuma tabbas ambaton Allah shi ne mafi girma. Kuma Allah Yana sane da abin da kuke aikatawa
Nawa nawa ne daga cikin zukata wadanda suka nesanta daga ambaton Allah ta’ala, har ya zamana sun yi sakayau sun kekashe. Amma kiran Allah Ubangiji bai gushe ba yana kwankwasa kofar kira zuwa ga a dawo... Shin lokacin da za su yi taushin ya yi? Fadakuwar_Zukata.