(Allah) Mai rahama.
Shi Ya koyar da Alqur’ani.
Ya halicci mutum .
Ya koyar da shi bayani.
Nuna katika
Ya ku waxanda suka yi imani ku nemi taimako ta hanyar haquri da salla. Lalle Allah Yana tare da masu haquri
Alkur’ani bai takaita a kan wani yare ko wasu mutane ba, A’a shi dai shiriya ne, kuma waraka ne ga dukkan wata zuciya mai yin imani, Duk wanda ya kawar da kai ga barinsa, to wata tazara mai nisa za ta kasance a tsakaninsa dashi wadda ba za a iya kaiwa karshenta ba. Alkur’ani_Shiriya ne_Ga talikai
Lalle wannan Alqur’anin yana shiryarwa ne ga (hanya) mafi miqewa, yana kuma yi wa muminai waxanda suke yin kyawawan ayyuka albishir cewa, lalle suna da lada mai girma
Alkur’ani ba littafi ne da ake karantawa ba kawai, A’a, an saukar dashi ne don a yi tuntuntuni game dashi...don haka duk wanda bai yi tuntuntunin ma’anoninsa ba, to kamar akwai wani rufi a kan zuciyarsa wanda ba za a iya bude shi ba. Tuntunin_Alkur’ani
A yayin da al’amura suka tsananta, kada ka tafi neman mafita a wani wuri a karen fari, a’a ka nemi mafaka ta hanyar komawa zuwa ga hakuri da salla, a cikinsu akwai samun dauki daga sama. #Hakuri_da salla
Gafala tana kekasar da zukata Ambaton Allah kuma yana tausasata ya kuma sa ta yin sabuwar rayuwa. Kada ka bari duniya ta tafiyar da kai_ka dawo yanzu-yanzu. Komawa_Zuwa ga_Allah