(Allah) Mai rahama.
Shi Ya koyar da Alqur’ani.
Ya halicci mutum .
Ya koyar da shi bayani.
Nuna katika
Yanzu ba za su yi tunani na basira ba (game da) Alqur’ani ba, ko kuwa akwai wani rufi ne a kan zukatansu?
Lalle wannan Alqur’anin yana shiryarwa ne ga (hanya) mafi miqewa, yana kuma yi wa muminai waxanda suke yin kyawawan ayyuka albishir cewa, lalle suna da lada mai girma
Ba don ado da neman albarka aka saukar da Alkur’ani ba kawai, A’a, sai dai an saukar da shi ne don mu fahimce shi, mu yi tuntuntuni game dashi, mu rayu a kan shiriyarsa a kan kowane irin gwadabe da muka bi. #Tuntuntuni Game da_Alkur’ani
Da Mun sanya shi Alqur’ani Ba’ajame da tabbas za su ce: “Me ya hana a bayyana ayoyinsa? Yanzu (a ce Alqur’ani) Ba’ajame (Annabi kuma) Balarabe?” Ka ce: “Shi ga waxanda suka yi imani shiriya ne da waraka. Waxanda kuwa ba sa yin imani akwai nauyi cikin kunnuwansu, shi kuma makanta ne a gare su.” Waxannan (sun yi kama da waxanda) ake kira daga wuri ma...
Kowace aya a cikin Alkur’ani tana dauke da wani muhimmin sako. Duk wanda ya sa hankalinsa da zuciyarsa game da ita (ayar), to zai fito da wani irin haske da kuma basira. #Hasken_Alkur’ani.
A yayin da al’amura suka tsananta, kada ka tafi neman mafita a wani wuri a karen fari, a’a ka nemi mafaka ta hanyar komawa zuwa ga hakuri da salla, a cikinsu akwai samun dauki daga sama. #Hakuri_da salla