(Allah) Mai rahama.
Shi Ya koyar da Alqur’ani.
Ya halicci mutum .
Ya koyar da shi bayani.
Nuna katika
Yanzu lokaci bai yi ba ga waxanda suka yi imani zukatansu su yi taushi da zikirin Allah da kuma abin da Ya saukar na gaskiya, kuma kada su zama kamar waxanda aka bai wa Littafi tun gabaninsu, sai lokaci ya tsawaita a gare su, sai zukatansu suka qeqashe; mafiya yawa kuma daga cikinsu fasiqai ne?
Kuma lalle za Mu jarrabe ku da wani abin tsoro da yunwa da tawayar dukiya da ta rayuka da ta ‘ya’yan itatuwa. Don haka ka yi albishir ga masu haquri
Alkur’ani yana shiryar da kai zuwa hanya mafi mikewa, Ba wai ta hanyar umarni da hani ba kawai, a’a a dukkan tsarin rayuwarka yana yi maka jagora zuwa ga rabauta da dacewa. Alkur’ani_Jagoran_Rayuwa#
Ya ku waxanda suka yi imani ku nemi taimako ta hanyar haquri da salla. Lalle Allah Yana tare da masu haquri
Kowace aya a cikin Alkur’ani tana dauke da wani muhimmin sako. Duk wanda ya sa hankalinsa da zuciyarsa game da ita (ayar), to zai fito da wani irin haske da kuma basira. #Hasken_Alkur’ani.
Ba don ado da neman albarka aka saukar da Alkur’ani ba kawai, A’a, sai dai an saukar da shi ne don mu fahimce shi, mu yi tuntuntuni game dashi, mu rayu a kan shiriyarsa a kan kowane irin gwadabe da muka bi. #Tuntuntuni Game da_Alkur’ani