(Allah) Mai rahama.
Shi Ya koyar da Alqur’ani.
Ya halicci mutum .
Ya koyar da shi bayani.
Nuna katika
Babu wani abin da ya fi ambaton Allah girma a duniya, Domin shi ne hasken zuciya, kuma tsawatarwar rai, kuma tsanin samun tabbatuwa. Duk lokacin da ka ambace shi (Allah) da gaskiya, to za ka zama ka kara samun kusanci dashi. #Ambaton_Allah_Shi ne mafi girma
Ba a yawaita magana yayin da ake cikin musiba, Ya isheka ka yi ta nanata fadin: “mu na Allah ne, kuma zuwa gare shi za mu koma” a cikin ranka. Domin a cikin fadar hakan akwai, mika wuya da yarda da kuma nutsuwa. #Mika wuya_da komawa.
Ka karanta abin da ake yi maka wahayinsa na Alqur’ani, ka kuma tsai da salla; lalle salla tana hana alfasha da kuma abin qi. Kuma tabbas ambaton Allah shi ne mafi girma. Kuma Allah Yana sane da abin da kuke aikatawa
Allah ba ya barin wanda ya yi hakuri A’a, yana kasancewa tare dashi yayin da yake cikin rauninsa da hawayensa, kuma a cikin kowace sujada akwai kyakkyawan fata. #Allah_Yana tare da_Masu Hakuri
Rufaffiyar zuciya ba za ta dosani hasken Alkur’ani ba. Mabudin kuma shi ne: Tadabburi da khushu’i da kuma neman gaskiya da gaske. Ka bude_Zuciyarka
Allah shi ne wanda ya halicci mutum, Kuma shi ne sanar da shi yadda zai yi magana ya isar da sako Shin muna amfani da ni’imar bayani cikin abin da zai yardar dashi? #Ni’imar_bayani