(Allah) Mai rahama.
Shi Ya koyar da Alqur’ani.
Ya halicci mutum .
Ya koyar da shi bayani.
Nuna katika
Zukata sune suke fahimta ba kunnuwa ba... Wanda ya bude wa gaskiya zuciyarsa, to zai samu haske a cikin Akur’ani, Wanda kuma ya rufeta, to ba zai taba saurara ba, ko da kuwa za a karanta masa ayoyi gaba dayansu. Zuciyoyi ne_Ke saurara
Lalle wannan Alqur’anin yana shiryarwa ne ga (hanya) mafi miqewa, yana kuma yi wa muminai waxanda suke yin kyawawan ayyuka albishir cewa, lalle suna da lada mai girma
Alkur’ani yana shiryar da kai zuwa hanya mafi mikewa, Ba wai ta hanyar umarni da hani ba kawai, a’a a dukkan tsarin rayuwarka yana yi maka jagora zuwa ga rabauta da dacewa. Alkur’ani_Jagoran_Rayuwa#
Ana karanta Alkur’ani ne don a tsarkake rai Salla kuma ana tsayar da ita ne don ta tsarkake yanayin mutum Duk wanda ya kiyaye wurin yi wa Ubangijinsa salla, to za ta tsare shi daga karkacewa. #Tasirin_Salla
Babu wani abin da ya fi ambaton Allah girma a duniya, Domin shi ne hasken zuciya, kuma tsawatarwar rai, kuma tsanin samun tabbatuwa. Duk lokacin da ka ambace shi (Allah) da gaskiya, to za ka zama ka kara samun kusanci dashi. #Ambaton_Allah_Shi ne mafi girma
(Su ne) waxanda idan wata musiba ta same su sai su ce: “Lalle mu na Allah ne, kuma lalle mu gare Shi muke komawa.”