(Allah) Mai rahama.
Shi Ya koyar da Alqur’ani.
Ya halicci mutum .
Ya koyar da shi bayani.
Nuna katika
Bushara mafi girma ga Muminai a cikin ‘yan kalmomi kawai take ba, A’a, a cikin alkawarin Allah take ta hanyar samu lada babba ga wanda ya bi hanyar nagarta. Busharar_Salihai
Alkur’ani ba littafi ne da ake karantawa ba kawai, A’a, an saukar dashi ne don a yi tuntuntuni game dashi...don haka duk wanda bai yi tuntuntunin ma’anoninsa ba, to kamar akwai wani rufi a kan zuciyarsa wanda ba za a iya bude shi ba. Tuntunin_Alkur’ani
Alkur’ani ya kasance shi ne ni’imar farko bayan rahama, Kuma ya zama kamar mafi girman abin da za a koyar da mutum bayan an halicce shi...shi ne maganar Allah. #Alkur’ani_Rahama
Jarabawoyi da Allah yake yi wa bayi, ba dalili ne da yake nuna fushin Ubangiji ba, a’a wata dama ce da masu hakuri suke samu don su daukaka. Tsoro da yunwa da rashi....dukkansu darussa ne na kara samun yarda da Allah. #Jarabta_da hakuri.
Yanzu lokaci bai yi ba ga waxanda suka yi imani zukatansu su yi taushi da zikirin Allah da kuma abin da Ya saukar na gaskiya, kuma kada su zama kamar waxanda aka bai wa Littafi tun gabaninsu, sai lokaci ya tsawaita a gare su, sai zukatansu suka qeqashe; mafiya yawa kuma daga cikinsu fasiqai ne?
Babu wani abin da ya fi ambaton Allah girma a duniya, Domin shi ne hasken zuciya, kuma tsawatarwar rai, kuma tsanin samun tabbatuwa. Duk lokacin da ka ambace shi (Allah) da gaskiya, to za ka zama ka kara samun kusanci dashi. #Ambaton_Allah_Shi ne mafi girma