(Allah) Mai rahama.
Shi Ya koyar da Alqur’ani.
Ya halicci mutum .
Ya koyar da shi bayani.
Nuna katika
Zukata sune suke fahimta ba kunnuwa ba... Wanda ya bude wa gaskiya zuciyarsa, to zai samu haske a cikin Akur’ani, Wanda kuma ya rufeta, to ba zai taba saurara ba, ko da kuwa za a karanta masa ayoyi gaba dayansu. Zuciyoyi ne_Ke saurara
Alkur’ani ba littafi ne da ake karantawa ba kawai, A’a, an saukar dashi ne don a yi tuntuntuni game dashi...don haka duk wanda bai yi tuntuntunin ma’anoninsa ba, to kamar akwai wani rufi a kan zuciyarsa wanda ba za a iya bude shi ba. Tuntunin_Alkur’ani
Nawa nawa ne daga cikin zukata wadanda suka nesanta daga ambaton Allah ta’ala, har ya zamana sun yi sakayau sun kekashe. Amma kiran Allah Ubangiji bai gushe ba yana kwankwasa kofar kira zuwa ga a dawo... Shin lokacin da za su yi taushin ya yi? Fadakuwar_Zukata.
Ka karanta abin da ake yi maka wahayinsa na Alqur’ani, ka kuma tsai da salla; lalle salla tana hana alfasha da kuma abin qi. Kuma tabbas ambaton Allah shi ne mafi girma. Kuma Allah Yana sane da abin da kuke aikatawa
Alkur’ani yana shiryar da kai zuwa hanya mafi mikewa, Ba wai ta hanyar umarni da hani ba kawai, a’a a dukkan tsarin rayuwarka yana yi maka jagora zuwa ga rabauta da dacewa. Alkur’ani_Jagoran_Rayuwa#
Dukkan wani rashi, dukkan wani bakin ciki, dukkan wata musiba... Duk irin yadda ta kai ga girma, za ta ci gaba da zama mai sauki idan ka tuna cewa kana hanyarka ce ta komawa zuwa ga mahiliccinka. #Musiba_da Hakuri