Sannan bayansu Muka mayar da ku madadinsu a bayan qasa don Mu ga me za ku aikata
Nuna katika
Lalle Mun bijiro da amana ga sammai da qasa da duwatsu sai suka qi xaukar ta suka ji tsoron ta, sai kuwa mutum ya xauke ta; lalle shi (mutum) ya kasance mai zaluntar kansa ne, mai jahilci
Don haka sai ka tsaya totar kamar yadda aka umarce ka kai da waxanda suka tuba tare da kai, kada kuwa ku wuce iyaka. Lalle Shi (Allah) Mai ganin abin da kuke aikatawa ne
Rayuwa mai dadi ba wai tana zuwa ne daga dukiya ko alfarma ba, a’a tana zuwa ne ta dalilin imani da ayyuaka nagari. Dukkan wani aiki nagari, karami ne ko babba, za a rubuta maka lada mai girma a wurin Allah idan ka aikata shi. #Rayuwa_Mai daxi
Halifanci a bayan kasa nauyi ne, ba karramawa ba ce kadai. An halicci mutum don ya gina duniya, ba don ya batata ba, don ya tsayar da adalci ba don ya zubar da jini ba. Ka zamo halifa na gaskiya kamar yadda Allah yake so ka zama. #Aikin_Mutum
Kuma ka tuna sa’adda Ubangijinka Ya ce da mala’iku: “Lalle ni zan sanya wani halifa a bayan qasa.” Suka ce: “Yanzu za Ka sanya mata wanda zai yi varna a cikinta kuma ya zubar da jini, alhali ga mu muna tasbihi tare da gode Maka, kuma muna tsarkake Ka?” (Allah) Ya ce: “Ni fa tabbas Na san abin da ku ba ku sani ba.”
Tsayuwa a kan imani yana baka aminci a zuciyarka da aminci a lahira, da kuma Aljannar da za a cika maka dukkan burikanka a lahira. Ka tuna; mala’iku fa na tare da kai a kowane lokaci. #Tsayuwa a kan_Imani