Sannan bayansu Muka mayar da ku madadinsu a bayan qasa don Mu ga me za ku aikata
Nuna katika
Amana nauyi ne mai girma da Allah ya bijirar dashi ga manyan halittu, amma suka ki yarda su karba, amma dan’adam yayi jara’a ya dauketa! Shin mun san kuwa hakikanin amanar da muka dauka a wuyayanmu? #Amana#
Halifanci a bayan kasa nauyi ne, ba karramawa ba ce kadai. An halicci mutum don ya gina duniya, ba don ya batata ba, don ya tsayar da adalci ba don ya zubar da jini ba. Ka zamo halifa na gaskiya kamar yadda Allah yake so ka zama. #Aikin_Mutum
Dukkan abin da ke sama da kasa horewar Allah ne garemu. Muyi kokari wurin neman arziqi, mu kuma gode wa ni’imominsa. Yin tuntuntuni cikin ayoyin Allah zai bude mana kofofin sanin kimar abubuwa da ilimi. #Tuntuntuni_a cikin_ Duniya
Kada ka wuce iyaka a cikin aikinka, lalle Allah ya ganin abin da kake aikatawa. Ka tsayu a kan abin da aka umarceka, da sannu za ka samu tsira a duniya da lahira. Tuba_Tsayuwa a kan tafarki madaidaici
Ba a bayar da Aljannar Firdaus sai ga wanda yayi imani yayi ayyuka nagari. Sakamako ne wanda ba za a iya kwatanta shi da dukiya ko matsayi ba. Lalle ita (Firdausi) Aljanna ce ta dawwama ga wanda ya kasance a kan tafarki ingantacce. #Aljannar_Firdaus
Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari to Aljannar Firdausi ita ce ta kasance masaukinsuSuna masu dawwama a cikinta, ba sa neman wani musaya da ita