Al Qur'ani Da Ci Gaban Al Ummah
See other videos from same category
Allah ne wanda Ya hore muku kogi don jiragen ruwa su riqa gudu a cikinsa da umarninsa, don kuma ku nema daga falalarsa don kuma ku gode
Lalle wannan Alqur’anin yana shiryarwa ne ga (hanya) mafi miqewa, yana kuma yi wa muminai waxanda suke yin kyawawan ayyuka albishir cewa, lalle suna da lada mai girma
Ya ku waxanda suka yi imani, an wajabta muku qisasi dangane da waxanda aka kashe; xa da xa, bawa da bawa, mace da mace[1]. To duk wanda aka yafe masa qisasin xan uwansa, to sai ya bibiye shi ta hanyar da ta dace, shi kuma ya biya diyyar ta hanyar kyautatawa. Wannan (abin da aka ambata), sauqi ne da rahama daga wajen Ubangijinku. Don haka duk wanda...
Manzanni ne masu albishir kuma masu gargaxi, domin kada mutane su sami wata hujja a wurin Allah bayan aiko manzannin. Kuma Allah Ya kasance Mabuwayi ne, Mai hikima
Ka ce da muminai maza su kame idanuwansu kuma su kiyaye farjinsu. Wannan shi ya fi tsarki a gare su. Lalle Allah Masanin abin da suke aikatawa ne Kuma ka ce da muminai mata su kame idanuwansu ] kuma su kiyaye farjinsu, kada kuma su fito da adonsu sai dai abin da ya bayyana daga gare shi ; kuma su sanya lulluvinsu a kan wuyan rigunansu[3]; kada kum...
Ya kai wannan Annabi, faxa wa matanka da ‘ya’yanka mata da kuma matan muminai (cewa) su sanya lulluvinsu. Wannan shi ya fi sanya wa a gane su, don kada a cuce su. Allah kuma Ya kasance Mai gafara ne, Mai rahama