Alƙur'ani Shi Ne Hanyar Haɓaka
See other videos from same category
Manzanni ne masu albishir kuma masu gargaxi, domin kada mutane su sami wata hujja a wurin Allah bayan aiko manzannin. Kuma Allah Ya kasance Mabuwayi ne, Mai hikima
To idan ba su amsa maka ba, to ka sani cewa ba abin da suke bi sai soye-soyen zukatansu kawai. Ba kuwa wanda ya fi vacewa kamar wanda ya bi son zuciyarsa ba tare da wata shiriya daga Allah ba. Lalle Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai
Yanzu mutum ba ya gani cewa Mu Muka halicce shi daga maniyyi, sai ga shi ya zama mai jayayya a fili?Ya kuma buga mana misali, kuma ya manta da halittarsa (yayin da) ya ce: “Wane ne zai raya qasusuwa, alhali kuma sun rududduge?Ka ce: “Wannan da Ya fare su tun farko Shi ne zai raya su; Shi kuwa Masanin kowacce irin halitta ne
Sannan lokacin da manzanninsu suka zo musu da (ayoyi) bayyanannu, sai suka nuna farin ciki da ilimin da ke gare su, abin kuma da suka kasance suna yi wa izgili ya saukar musu To lokacin da suka ga azabarmu sai suka ce: “Mun yi imani da Allah Shi kaxai, mun kuma kafirce wa abin da muka kasance muna yin shirka da shi.” To imaninsu bai zamanto zai a...
Lalle a cikin halittar sammai da qasa da sassavawar dare da rana da jiragen ruwa da suke tafiya a kan ruwa da abin da yake amfanar mutane da kuma abin da Allah Ya saukar daga sama na ruwa, Ya rayar da qasa da shi bayan mutuwarta, Ya kuma yaxa duk wata halitta mai tafiya a cikin (qasa) da jujjuyawar iska, da kuma girgije da aka hore shi tsakanin sam...
Ya kuma hore muku abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa gaba xayansu daga gare Shi. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga mutanen da suke yin tunani