Wannan bayani ne don mutane, kuma shiriya ce da kuma wa’azi ga masu taqawa
Nuna katika
“Kaicona ina ma da ban riqi wane aboki ba!“Haqiqa ya vatar da ni daga bin Alqur’ani, bayan ya zo mini.” Shaixan kuwa ya kasance mai tavar da mutum neManzo kuma ya ce: “Ya Ubangijina, lalle mutanena sun riqi wannan Alqur’ani abin qaurace wa
Ba lallai ne kana da bukatuwa zuwa ga dogon wa’azi ba, Aya guda daya....da ta dace da zuciyar da ta shirya karbar gaskiya, sai ta canja ta. #Farkawar_zuciya
Allah Shi ne Majivincin lamarin waxanda suka yi imani, Yana fitar da su daga duffai zuwa ga haske; waxanda suka kafirce kuwa, majivinta lamarinsu su ne xagutai, suna fitar da su daga haske zuwa duffai. Waxannan su ne ‘yan wuta; su masu dawwama ne a cikinta
Ya isheka ka san cewa a gaba gareka akwai wani littafi daga Allah... Wanda yake cike da gaskiya da rahama da bayani. #Zancen_Allah
Alqur’ani ba ya zuwar maka da wani tunani da za ka warware shi, a’a sai dai shi kamar boyayyan sauti ne da yake raya abin da ka yi zaton ya mutu a zuciyarka. #Sautin_Alqur’ani
Muminai na haqiqa (su ne) kaxai waxanda idan aka ambaci Allah, sai zukatansu su raurawa, idan kuma aka karanta musu ayoyinsa, sai su qara musu imani, kuma ga Ubangijinsu ne kawai suke dogara