(Allah Ya ce da su): “Ko kuna tsammani ne cewa Mun halicce ku ne ba manufa”. [Mu’uminun: 115]
Nuna katika
Duk wata gasa da za a buga, to tana da manufa. To yanzu zai yiwu a hankalce rayuwar mutum ta zamo ba tare da wata manufa ba?
Duniya ta sa ido tana kallon ‘yan wasa a gasar cin kofin duniya…sai dai shi kuma Alqur’ani yana so ne da ka yi duba zuwa ga kanka a karan-fari. Yana so ka yi duba zuwa ga zuciyarka da tsoron ka da kuma duba zuwa ga tambayoyin da ke cikin ranka waxanda ba mai iya ganinsu.
“Lalle tsanani yana tare da sauqi” [Sharh: 6]
“Ku saurara, da ambaton Allah ne zukata suke nutsuwa”. Ra’ad: 28
Alqur’ani yana tunatar da mutum wani abu da yake mantawa da shi yayin da yake tsaka a cikin wasu shagulgula: lallai tafiyar gajera ce...kuma ma’anar abu ta fi hayaniya muhimmanci.#Hasken_Alqur’ani#Mahanga#Tafiyar_rayuwa#Kofin_duniya#Musulunci
A cikin kowace gasa ana shan wahala kafin a kai qarshe, haka ma al’amarin yake game da rayuwa. Ita kuma zuciya tana neman abin da zai ba ta nutsuwa ta haqiqa ne. #Hasken_Alqur’ani#Zaman_lafiya#Qwallon_qafa#Ayar_Alqur’ani#Nutsuwar_Zuciya