“Ku saurara, da ambaton Allah ne zukata suke nutsuwa”. Ra’ad: 28
Nuna katika
Yayin da ake cikin hayaniyar jama’a....to akwai wani sauti da yake can cikin ranka wanda babu mai iya jin sa in ba kai ba. Don haka Alqur’ani yana magana ne da wannan vangaren mai zurfi da yake cikin ran mutum. #Hasken_Alqur’ani #Gasar_cin_kofin_duniya #Alqur’an #Dan’adamtaka #Musulunci
Mutum ya fi qarfin a wulaqanta shi saboda jinsin da ya fito ko launinsa ko garin da ya fito. Darajarsa ta haqiqa ta fi dukkan wani rabe-rabe da za a yi. #Hasken_Alqur’ani#Mutunci_xan’adam#Kofin_duniya#Saqon_Musulunci#Xan’adamtaka
Alqur’ani yana tunatar da mutum wani abu da yake mantawa da shi yayin da yake tsaka a cikin wasu shagulgula: lallai tafiyar gajera ce...kuma ma’anar abu ta fi hayaniya muhimmanci.#Hasken_Alqur’ani#Mahanga#Tafiyar_rayuwa#Kofin_duniya#Musulunci
“Da kuma cikin kawunanku. Yanzu ba kwa lura ba? Zariyat: 21
Wasu nasarorin ba sa zuwa da gaggawa. Hakanan yayin da ake rayuwa, haquri wani yanki ne na tafiyar da ake kan yinta. #Hasken_Alqur’ani#Haquri#Imani#qwallon_qafa#Ayar_Alqur’ani
A gasar kofin duniya ana samun bambancin launukan mutane da yaruka da kuma garuruwa, sai dai kuma dukkanninsu suna nan a matsayin su na mutane ‘yan’adam.Don haka Alqur’ani yana tunatar da mu game da darajar kowane irin mutum.