Imani Da Gaibu A Musulunci
See other videos from same category
Waxanda kuma ba su sami wadatar yin aure ba su kame kansu har Allah Ya wadata su daga falalarsa. Waxanda kuwa suke neman fansar kansu daga bayinku[1], sai ku ba su damar fansar kansu, idan kun san suna da halin iya biya; kuma ku ba su wani abu daga dukiyar Allah da Ya ba ku. Kada kuma ku tilasta wa kuyanginku ‘yan mata a kan yin zina idan sun nemi...
Ta yaya?! (haka zai faru) alhali idan suka yi nasara a kanku ba za su duba wani kusanci ba balle wani alqawari game da ku? Suna yardar da ku ne da bakunansu, alhali kuwa zukatansu suna qi. Yawancinsu kuma fasiqai ne
Ka ce: “Da falalar Allah da rahamarsa, sai su yi farin ciki da wannan; shi ya fi alheri daga abin da suke tarawa (na dukiya).”
Ya ku mutane, ku kiyaye dokokin Ubangijinku Wanda Ya halicce ku daga rai guda xaya, kuma Ya halicci matarsa daga shi, kuma Ya yaxa maza da mata masu yawa daga gare su. Kuma ku kiyaye dokokin Allah Wanda kuke yi wa juna magiya da Shi, kuma ku kiyaye (yanke) zumunci. Lalle Allah Mai kula da ku ne
Ka kuma ce da bayina su faxi (magana) wadda ita ce ta fi kyau. Lalle Shaixan yana vata tsakaninsu. Lalle Shaixan ya tabbata maqiyi ne mai bayyana (qiyayya) ga mutum
Idan kuma suka haxu da waxanda suka yi imani sai su ce: “Mun yi imani.” To amma idan suka kevanta da shaixanunsu (iyayen gidansu)[1] sai su ce: “Mu fa lalle muna nan tare da ku, mu kawai izgili ne muke yi.” Allah Yana yi musu izgili, kuma Yana yi musu talala cikin shisshiginsu suna masu ximuwa