Alhakin Zumunci A Musulunci
See other videos from same category
Idan munafukai suka zo maka sai suka ce: “Muna shaidawa cewa lalle kai Manzon Allah ne.” Allah kuma Yana sane da cewa kai tabbas Manzonsa ne, kuma Allah Yana shaidawa cewa munafukai tabbas qarya suke yi
Ba ka ga waxanda suka yi munafunci suna ce wa ‘yan’uwansu waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi: “Tabbas idan aka fitar da ku, lalle za mu fita tare da ku, ba kuma za mu bi wani mutum game da ku ba har adaba, kuma idan aka yaqe ku tabbas za mu taimake ku.” Allah kuma Ya san tabbas qarya suke yi
Idan kuma suka haxu da waxanda suka yi imani sai su ce: “Mun yi imani.” To amma idan suka kevanta da shaixanunsu (iyayen gidansu)[1] sai su ce: “Mu fa lalle muna nan tare da ku, mu kawai izgili ne muke yi.” Allah Yana yi musu izgili, kuma Yana yi musu talala cikin shisshiginsu suna masu ximuwa
Kuma ka tuna lokacin da Muka xauki alqwari daga Banu Isra’ila cewa, ba za ku bauta wa kowa ba sai Allah, kuma za ku kyautata wa iyaye da makusanta da marayu da miskinai, kuma ku riqa yi wa mutane kyakkyawar magana, kuma ku tsai da salla, kuma ku ba da zakka, sannan sai kuka ba da baya sai ‘yan kaxan daga cikinku, alhalin kuna masu bijirewa
Kuma ku bauta wa Allah (Shi kaxai), kada ku haxa Shi da komai; kuma ku kyautata wa iyaye da dangi makusanta da marayu da talakawa da maqwabci makusanci da maqwabci na nesa, da abokin da ake tare[1] da kuma matafiyi da bayinku. Lalle Allah ba Ya son duk wanda ya kasance mai taqama, mai yawan fariya
Ya ku mutane, lalle Mu Muka halicce ku daga namiji da mace, Muka kuma sanya ku al’ummu da qabilu don ku san juna. Lalle mafi girmanku a wurin Allah shi ne wanda ya fi ku taqawa. Lalle Allah Masanin sarari ne, Masanin voye