Ka yi riqo da afuwa, kuma ka yi umarni da kyakkyawan abu, ka kuma kawar da kai daga wawaye
Nuna katika
Allah ya la'anci waɗanda ba su hana mummunan aiki, don haka mu dauki nauyin fuskantar da wasu zuwa alheri da hana sharri. #Alhakin_Zamantakewa #Kiran_Zuwa_Ga_Alheri
Lokacin da mutane suka fuskanci barna a bayan kasa, suna neman mafita ta zahiri, kamar shingen da Zul-Qarnayn ya gina. Mu koyi wannan hikimar." #Mafita_Na_Zahiri #Hikima
A lokacin da mutane suka gafala daga ambaton Allah, to azaba na iya samunsu alhali suna cikin gafala, don haka a ko da yaushe zuciyoyinmu su zama a halarce da ambaton Allah. #Tunatarwa_Ta Addini
Waxannan su ne ake saka wa da xakuna na Aljanna saboda haqurin da suka yi, za kuma a tare su a cikinta da gaisuwa da sallama
“Kuma ya ku mutanena, ba na tambayar ku wata dukiya a kansa (kiran); ladana a wurin Allah kawai yake. Ni kuwa ba zan kori waxanda suka yi imani ba. Lalle su masu saduwa ne da Ubangijinsu, sai dai ni ina ganin ku mutane ne da kuke jahiltar (gaskiya).”
Idan kuma suka ji maganar banza sai su kau da kai daga gare ta, sai kuma su ce: “(Sakamakon) ayyukanmu yana gare mu, ku kuma na ayyukanku yana gare ku, kun kuvuta daga gare mu, ba ruwanmu da wawaye!”