Al Qur'ani Da Ci Gaban Al Ummah
See other videos from same category
Lalle waxanda suke kafirce wa Allah da manzanninsa, kuma suke nufin su nuna bambanci tsakanin Allah da manzanninsa, kuma suna cewa: “Mun yi imani da wasu, mun kuma kafirce wa wasu,” kuma suna son su riqi wani tafarki tsakanin wannan (imani da kafirci) Waxannan su ne kafirai na haqiqa. Kuma Mun yi wa kafirai tanadin wata azaba mai wulaqantarwa
Ya ku waxanda suka yi imani, an wajabta muku qisasi dangane da waxanda aka kashe; xa da xa, bawa da bawa, mace da mace[1]. To duk wanda aka yafe masa qisasin xan uwansa, to sai ya bibiye shi ta hanyar da ta dace, shi kuma ya biya diyyar ta hanyar kyautatawa. Wannan (abin da aka ambata), sauqi ne da rahama daga wajen Ubangijinku. Don haka duk wanda...
Lalle wannan Alqur’anin yana shiryarwa ne ga (hanya) mafi miqewa, yana kuma yi wa muminai waxanda suke yin kyawawan ayyuka albishir cewa, lalle suna da lada mai girma
Manzanni ne masu albishir kuma masu gargaxi, domin kada mutane su sami wata hujja a wurin Allah bayan aiko manzannin. Kuma Allah Ya kasance Mabuwayi ne, Mai hikima
Allah kuwa Ya yi wa waxanda suka yi imani daga cikinku suka kuma yi aiki na gari alqawarin lalle zai sanya su halifofi a bayan qasa kamar yadda Ya sanya waxanda suke gabaninsu halifofi, kuma lalle zai tabbatar musu da addininsu wanda Ya yardar musu, tabbas kuma zai dawo musu da zaman lafiya bayan zamantowarsu cikin tsoro. Su bauta mini, ba sa yin s...
Bambanci Tsakanin Maganin Al Qur'ani Da Maganin Yammacin Don Matsalolin Al'umma