Kyakkyawan Fatan da Kuma Tsoro
See other videos from same category
Muhammadu Manzon Allah ne. Waxanda kuma suke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai, kuma masu tausayin junansu ne; za ka gan su suna ruku’i suna sujjada suna neman falala daga Allah da yardarsa; alamominsu na gurbin sujjada suna bayyana a fuskokinsu. Wannan shi ne misalinsu a cikin Attaura. Misalinsu kuwa a cikin Linjila kamar shuka ce da ta fi...
Ubangijinku kuma Ya ce: “Ku roqe Ni zan amsa muku. Lalle waxanda suke yin girman kai game da bauta min, ba da daxewa ba za su shiga Jahannama a wulaqance.” Allah ne wanda Ya halitta muku dare don ku natsu a cikinsa, rana kuma don ku ga (yadda za ku yi harka). Lalle Allah Mai falala ne ga mutane, sai dai kuma yawancinsu ba sa godewa
Kuma ku yi gaggawa zuwa ga neman gafara ta musamman daga wajen Ubangijinku, da kuma Aljanna wadda faxinta yake daidai da sammai da qasa, an yi tanadinta domin masu taqawa (Su ne) waxanda suke ciyarwa a cikin halin yalwa da halin qunci, kuma masu voye fushi kuma masu yin afuwa ga mutane. Allah kuwa Yana son masu kyautatawa
Alkawurra da Gargadi
Waxanda suka zauna a gida daga cikin muminai ba su fita yaqi ba, in dai ba masu larura ba, ba za su yi daidai da masu jihadi don xaukaka kalmar Allah da dukiyoyinsu da kawunansu ba. Allah Ya fifita darajar masu jihadi da dukiyoyinsu da kawunansu a kan waxanda suka zauna a gida. Kuma dukkansu Allah Ya yi masu alqawarin Aljanna. Kuma Allah Ya fifita...
Kuma al’amarinmu bai zamanto ba face kalma xaya kamar qiftawar idoHaqiqa kuma Mun hallakar da ire-irenku , to ko akwai mai wa’azantuwa?Kuma kowane abu da suka aikata yana cikin littattafaiKowane qaramin abu da babba kuma suna nan a rubuceLalle masu taqawa suna cikin gidajen Aljanna da qoramu