A lokacin da gaskiya ta bayyana bayan lokaci ya qure, ba abin da zai rage sai nadama.
Ka tuna cewa imani ba ya amfani bayan jarabawa ta qare, don haka ka yi gaggawa tun yanzu kafin ka
“Da kuwa za ka ga lokacin da masu manyan laifuka suke sunkuye da kawunansu a wurin Ubangiijnsu (suna cewa): “Ya Ubangijinmu, mun gani, mun kuma ji, to Ka mayar da mu (duniya), za mu yi aiki nagari, haqiqa mu masu sakankancewa ne.” (Sajada: 12)
A lokacin da gaskiya ta bayyana bayan lokaci ya qure, ba abin da zai rage sai nadama.
Ka tuna cewa imani ba ya amfani bayan jarabawa ta qare, don haka ka yi gaggawa tun yanzu kafin ka ce “Ina ma! (da na sani).”
“Da kuwa za ka ga lokacin da masu manyan laifuka suke sunkuye da kawunansu a wurin Ubangiijnsu (suna cewa): “Ya Ubangijinmu, mun gani, mun kuma ji, to Ka mayar da mu (duniya), za mu yi aiki nagari, haqiqa mu masu sakankancewa ne.” (Sajada: 12)
Wani lokaci zai zo da kowane mutum zai ga gaskiya a bayyane, amma kuma dama ta qare a daidai wannan lokacin.
Yaqini na gaskiya shi ne ka yi imani kafin an tilasta maka yin imani.
“Aka kuma busa qaho, sai ga su suna fitowa daga qaburbura zuwa wurin Ubangijinsu. Suka ce: “Kaiconmu, wane ne ya tashe mu daga makwancinmu?” (Sai a ce da su): “Ai wannnan shi ne abin da (Allah) Mai rahama Ya yi alqawarinsa, manzanni kuma sun yi gaskiya.” (Suratu Yasin: 51-52)
Rana ce da abin da zai faru babu wanda yake tsammaninsa, za a tashi mutane daga qaburburansu, kuma su yi tambaya: “Wa ya tashe mu?”
Tunatarwa game da qarfin Allah da ikonsa a ranar da nadama ba ta da amfani.
“Aka kuma busa qaho, sai ga su suna fitowa daga qaburbura zuwa wurin Ubangijinsu. Suka ce: “Kaiconmu, wane ne ya tashe mu daga makwancinmu?” (Sai a ce da su): “Ai wannnan shi ne abin da (Allah) Mai rahama Ya yi alqawarinsa, manzanni kuma sun yi gaskiya.” (Suratu Yasin: 51-52)
A lokaci xaya Allah zai rayar da matattu, Ya bayyanar mana da alqawarinsa da ba a savawa.
Mu yi duba zuwa ga ayyukanmu tun yanzu kafin mu kasance cikin wannan ranar.
“Har sai idan da mutuwa ta zo wa xayansu zai ce: “Ubangijina, Ku mai da ni (duniya) mana. “Don in yi aiki na gari game da abin da na bari (a rayuwata).” Ina! Lalle wannan kalma ce da yake faxin ta (da bakinsa). A gabansu kuwa akwai shamaki har zuwa ranar tashinsu.” (Suratul Muminun: 99-100).
A lokacin da mutuwa take kusantowa, mutum ya kan yi burin a dawo da shi domin ya yi kyakkyawan aiki, amma dama ta kuvuce.
Lokaci yana da tsada, kar ka jira har sai lokacin Alqiyama ya yi.
“Har sai idan da mutuwa ta zo wa xayansu zai ce: “Ubangijina, Ku mai da ni (duniya) mana. “Don in yi aiki na gari game da abin da na bari (a rayuwata).” Ina! Lalle wannan kalma ce da yake faxin ta (da bakinsa). A gabansu kuwa akwai shamaki har zuwa ranar tashinsu.” (Suratul Muminun: 99-100).
Wane ne zai yi burin a dawo da shi don ya gyara makomarsa a lahira?!
Rayuwa dama ce da ba a maye gurbinta in ta kuvuce.
Aikinka a yau shi ne zai tantance makomarka a ranar da aka yi alqawari (alqiyama)
“Idan kuma aka ce musu: “Kada ku yi varna a bayan qasa”, sai su ce: “Mu fa masu gyara ne kawai.” Saurara, lalle su su ne mavarnata, amma ba sa jin hakan.” (Baqara: 11-12)
A daidai lokacin da wasu suke da’awar cewa su masu gyara ne alhali kuma su mavarnata ne, to gaskiya za ta bayyana ga waxanda suke tadabburi (tuntuntuni)
“Idan kuma aka ce musu: “Kada ku yi varna a bayan qasa”, sai su ce: “Mu fa masu gyara ne kawai.” Saurara, lalle su su ne mavarnata, amma ba sa jin hakan.” (Baqara: 11-12)
Kada ka yi da'awar gyara alhali kana shuka varna.
Wajibi ne mutum ya yi nazari a cikin ayyukan da yake yi kafin ya gamsar da kansa cewar abin da yake yi alheri ne.
“... kada ka bi son zuciya sai ya vatar da kai daga hanyar Allah. Lalle waxanda suke vacewa daga hanyar Allah suna da (sakamakon) azaba mai tsanani saboda mantawar da suka yi da ranar hisabi.” (Surat Sad: 26)
Bin son zuciya kan iya sakawa ka yi nisa daga miqaqqiyar hanya, kar ka bari abin da kake so ya ja ka zuwa vata.
Lahira hisabi da uquba za a yi, don haka ka zama a faxake.
“... kada ka bi son zuciya sai ya vatar da kai daga hanyar Allah. Lalle waxanda suke vacewa daga hanyar Allah suna da (sakamakon) azaba mai tsanani saboda mantawar da suka yi da ranar hisabi.” (Surat Sad: 26)
Son zuciya zai iya zama dalilin vata, don haka kar ka manta ranar hisabi.
Ka yi rayuwa daidai da abin da zai yardar da Allah don ka samu tsira a duniya da Lahira.
“Ka karanta abin da ake yi maka wahayinsa na Alqur’ani, ka kuma tsai da salla; lalle salla tana hana alfasha da kuma abin qi. Kuma tabbas ambaton Allah shi ne mafi girma. Kuma Allah Yana sane da abin da kuke aikatawa.” (Suratul Ankabut: 45)
Alqur'ani da salla suna cikin ibadu masu tasiri a rayuwarmu, domin suna haskaka hanya, ita kuma salla ta kevanta da cewa tana hana mu alfasha da munkari.
Ibadar zikiri kuma ita ce ta ke girmama zuciya, take kuma haxa ta da Allah.
“Ka karanta abin da ake yi maka wahayinsa na Alqur’ani, ka kuma tsai da salla; lalle salla tana hana alfasha da kuma abin qi. Kuma tabbas ambaton Allah shi ne mafi girma. Kuma Allah Yana sane da abin da kuke aikatawa.” (Suratul Ankabut: 45)
Salla ba wai ibada ce kawai ba, a’a wata garkuwa ce da take kare mu daga faxawa cikin savon Allah.
“Haqiqa akwai izina a cikin labaransu (annabawa) ga ma’abota hankali. (Alqur’ani) bai zamanto zance ne da ake qirqirar sa ba, sai dai zance ne da yake gaskata abin da ya rigaye shi (na littattafai), da kuma bayanin komai; shiriya ne kuma da rahama ga mutanen da suke yin imani.” (Yusuf: 111)
A cikin labaran annabawa akwai izina a gare mu gaba xaya, tunatarwa ce don tuntuntuni da kuma koyo daga rayuwar waxanda Suka gabace mu.
Alqur'ani ba labarai ba ne kaxai, a’a Alqur’ani gaskatawa ne da shiriya da rahama.
“Haqiqa akwai izina a cikin labaransu (annabawa) ga ma’abota hankali. (Alqur’ani) bai zamanto zance ne da ake qirqirar sa ba, sai dai zance ne da yake gaskata abin da ya rigaye shi (na littattafai), da kuma bayanin komai; shiriya ne kuma da rahama ga mutanen da suke yin imani.” (Yusuf: 111)
Duk wata qissa a cikin Alqur’ani tana xauke da darussa na haqiqa a rayuwa.
Ga wanda ya yi imani da Allah, za ka samu a cikin kowace aya akwai shiriya da rahama.
“Kowanne (cikin al’ummun da suka gabata) Mun kama shi da laifinsa; daga cikinsu akwai waxanda Muka aiko wa da duwatsu, akwai kuma waxanda tsawa ta kama su, kuma daga cikinsu akwai waxanda Muka kifar da su cikin qasa, akwai kuma daga cikinsu waxanda Muka nutsar a ruwa. Allah kuma bai kasance Yana zaluntar su ba, sai dai kawai kawunansu suke zalunta.” (Ankabut: 40
Kowace rai za ta girbi abin da ta aikata, kuma uqubobin da suke aukuwa a duniya ba komai ba ne face sakamakon zaluncin xan’adam ga kansa.
Allah ba ya zaluntar kowa, amma mutane suna zaluntar kawunansu.
“Kowanne (cikin al’ummun da suka gabata) Mun kama shi da laifinsa; daga cikinsu akwai waxanda Muka aiko wa da duwatsu, akwai kuma waxanda tsawa ta kama su, kuma daga cikinsu akwai waxanda Muka kifar da su cikin qasa, akwai kuma daga cikinsu waxanda Muka nutsar a ruwa. Allah kuma bai kasance Yana zaluntar su ba, sai dai kawai kawunansu suke zalunta.” (Ankabut: 40
Sakamako yana zuwa me daidai da aiki, abin da ka shuka shi za ka girba.
Ka yi dogon tunani game da makomar waxanda suka juya wa gaskiya baya, kuma ka xau darasi daga cikin rayuwarsu da ta shuxe.
Muna labarta maka kowanne daga labarun manzanni, abin da za Mu kwantar da zuciyarka da shi. Gaskiya kuwa ta zo maka cikin wannan (Surar) da izina da gargaxi ga muminai. (Hud: 120)
Qissoshin annabawa ba wai kawai hikayoyi ba ne, a'a darussa ne da suke tabbatar da zuciya, kuma suke haskaka hanya.
Kowace gaskiya da wa'azi da suke cikin kowace qissa tunatarwa ce ga muminai.
Muna labarta maka kowanne daga labarun manzanni, abin da za Mu kwantar da zuciyarka da shi. Gaskiya kuwa ta zo maka cikin wannan (Surar) da izina da gargaxi ga muminai. (Hud: 120)
A duk wani labari cikin labaran annabawa za mu samu abin da zai qara tabbatar da imani kuma ya shiryar da zuciyoyi.
Alqur’ani tunatarwa ce da kuma haske ga muminai a kowane zamani.